Dangote Ya Bude Kofar Sayar Da Hannun Jari A Matatarsa Ga Talakawa

Aliko Dangote ya fara sayar da hannun jari sama da biliyan 4.1 a matatar man fetur dinsa ga jama'a, inda kowane hannun jari zai kai Naira 525, a wani shiri da za a iya samun sama da Naira tiriliyan 2.

Satumba 19, 2026 - 04:25
0 1
Dangote Ya Bude Kofar Sayar Da Hannun Jari A Matatarsa Ga Talakawa
Hoto: FrankvEck / Wikimedia Commons (CC BY-SA 4.0) - matatar Dangote a lokacin gini

Alhaji Aliko Dangote ya fara sayar da hannun jari sama da biliyan 4.1 a matatar man fetur dinsa ga talakawan Najeriya, inda kowane hannun jari zai kai Naira 525, kuma mafi karancin hannun jarin da za a saya shi ne guda 10.

Shirin, wanda zai gudana daga ranar 14 ga Satumba har zuwa 13 ga Oktoba, 2026, ana sa ran zai kawo sama da Naira tiriliyan 2 wa kamfanin. Darajar hannun jarin da ake sayarwa ta kai kimanin dala biliyan 1.6, yayin da darajar matatar baki daya ta kai kimanin dala biliyan 49.

Dangote ya ce manufar wannan shiri ita ce ba wa direbobi, ma'aikata, da 'yan kasuwa damar mallakar wani bangare na matatar, yana mai cewa cewa muna son tabbatar da direbobinmu, ma'aikatanmu, manajoji, da kowa ya samu damar mallakar wani bangare na wannan matatar.

A cewar rahotanni, masu saye hannun jarin na iya samun kason ribar shekara-shekara (dividend) a dala nan gaba.

Menene Ra'ayinka?

So So 0
Ƙin so Ƙin so 0
So So 0
Ban Dariya Ban Dariya 0
Mamaki Mamaki 0
Baƙin Ciki Baƙin Ciki 0
Fushi Fushi 0

Sharhohi (0)

User